[ad_1]
Gwamnatin jihar Sokoto ta raba kuɗi naira miliyan ₦14.68 domin sayan shanun sallah ga marayun dake gundumomi 88 dake jihar.
A cewar shugaban hukumar Zakka ta jihar, Mallam Lawal Maidoki ya ce an ɗauki matakin ne domin suma su yi bikin sallah cikin walwala kamar sauran yara.
Ya ce kowace gunduma zata karbi kuɗin da ba su gaza ₦160000 domin su sayi saniya su yanka kana su raba naman ga marayun dake gundumar.
Anasa jawabin mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya yabawa hakimai kan sadaukarwar da suka nuna wajen tabbatar da shirin ya samu na nasara a yankunansu.
[ad_2]