Gwamnatin jihar Niger ta fara raba tallafin shinkafa mai saukin farashi ga mazauna jihar.
Da yake magana da yan jarida a Minna ranar Asabar, Mustapha Jibrin shugaban kwamitin rabon tallafin a mazabar Tudun Wada south ya ce tallafin kayan da kudinsu ya kai miliyan 20 aka raba a mazabar.
Jibrin wanda ya samu wakilcin Sirajo Sama’ila ya ce mazabar ta kunshi akwatun zabe 50 kuma ita ce mafi girma a karamar hukumar Chanchanga ta jihar.
“mazabar ita tafi yawan tashoshin zabe, mun yarda cewa gidaje 70 daga kowace akwatun zabe za su amfana” ya ce.
Ya ce an yi haka ne saboda tallafin ba zai ishi a bawa kowa ba duk da cewa mai yawa aka saya.
Shugaban ya yabawa kokarin gwamnatin tarayya da kuma ta jiha kan amincewa da rabon tallafin domin rage raÉ—aÉ—in cire tallafin cire man fetur.