Gwamnatin Enugu ta bayyana dalilin sanya haraji kan gawar mutane

Gwamnatin Jihar Enugu a ranar Lahadi tayi ƙarin haske kan matakin da ta ɗauka kan sanya haraji akan gawar mutane dake ajiye a ɗakin ajiye gawarwaki dake jihar.

Gwamnatin ta ce anyi yunkurin karbar harajin ne bawai dan  saboda gwamnati tana son tara kuÉ—i ba.

Shugaban hukumar tattara kuÉ—aÉ—en shiga ta jihar Enugu, Emmanuel Nnamani lokacin da yake mayar da martani kan takardar harajin da aka aikawa gidajen ajiye gawa dake jihar wacce ake ta ce-ce-kuce akai a kafafen sadarwar zamani.

A cewarsa harajin na cikin ƙudirin dokar Harajin Gidajen Ajiye Gawa dake jihar da ta daɗe ana amfani da ita kuma ba sabon abu ba ne a jihar.

Nnamani ya bayyana cewa ₦40 za a riƙa biya kowace rana akan kowace gawa.

“Haraji ne ba na kai tsaye ba da masu gidajen ajiye gawa za su rika biya ba wai iyalin mamaci ba kuma ₦40 ne kawai ba ₦40,000 ba tun lokaci da aka fito da harajin babu wanda aka hana binne gawarsa,” ya ce.

“Hakan na nufin idan gawa ta yi kwana 100 ana sa ran gidan ajiye gawar zai biya gwamnati ₦4000.”

More News

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta É—auki hanyar warware rikicin jam’iyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban Æ™ungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...