Gwamnatin Edo ta bayar da umarnin gudanar da bincike kan kisan mafarauta a garin Uromi

Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan mafarautan da aka yiwa kisan gilla akan hanyarsu ta zuwa gida bikin sallah.

Wasu fusatattun matasa ne suka tsare mutanen a motar da suke ciki a garin Uromi dake ƙaramar hukumar Esan North East ta jihar Edo.

Bayan da suka caje motar da suke ciki dandazon ɓatagarin matasan sun gano bindigar farauta inda daga nan suka yanke hukuncin cewa mutanen masu garkuwa da mutane ne inda suka ƙone su da ransu.

Wani fefan bidiyo da ya karaɗe soshiyal midiya ya nuna wasu matasa na tattara mamatan kafin su saka musu wuta.

Gwamna Okphebolo  ya ci alwashin gurfanar da wadanda suka aikata kisan kan a gaban shari’a.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Uromi ta bakin babban jami’in tsaron gidan gwamnatin jihar, SP Solomon Osaghale  ya ce yake wurin ne domin duba irin girman ɓarnar tare da tabbatar da an gudanar da cikakken bincike.

More from this stream

Recomended