Gwamnatin Buhari gwamnati ce ta makaryata acewar Atiku

[ad_1]








Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayyana gwamnati mai ci da shugaba Buhari yake jagoranta a matsayin gwamnatin makaryata.

Toshon mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ranar Alhamis lokacin da yakewa mambobin jam’iyar PDP jawabi a Enugu.

Mai neman tsayawa takarar shugaban kasar ya ce jam’iyar APC ta yi alkawarin samar da ayyukan yi miliyan uku a kowace shekara amma ƙasar nan kullum karuwar rashin aikin yi ake samu da ya jawo mummunan rashin tsaro.

“Wannan gwamnatin, gwamnati ce ta makaryata sun yi alkawarin samar da ayyukan yi miliyan uku a shekara amma yan Najeriya suna rasa ayyukan yi miliyan uku a kowace shekara,”ya ce.

“Wannan rasa ayyuka ya haifar da mummunan yanayin rashin tsaro, Najeriya na cikin wani yanayi mai dauke da kalubale. A yau tattalin arziki na cikin mawuyacin hali kalubale mafi girma shine na rashin aikin yi.”




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...