Gwamnatin Buhari gwamnati ce ta makaryata acewar Atiku

[ad_1]








Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayyana gwamnati mai ci da shugaba Buhari yake jagoranta a matsayin gwamnatin makaryata.

Toshon mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ranar Alhamis lokacin da yakewa mambobin jam’iyar PDP jawabi a Enugu.

Mai neman tsayawa takarar shugaban kasar ya ce jam’iyar APC ta yi alkawarin samar da ayyukan yi miliyan uku a kowace shekara amma ƙasar nan kullum karuwar rashin aikin yi ake samu da ya jawo mummunan rashin tsaro.

“Wannan gwamnatin, gwamnati ce ta makaryata sun yi alkawarin samar da ayyukan yi miliyan uku a shekara amma yan Najeriya suna rasa ayyukan yi miliyan uku a kowace shekara,”ya ce.

“Wannan rasa ayyuka ya haifar da mummunan yanayin rashin tsaro, Najeriya na cikin wani yanayi mai dauke da kalubale. A yau tattalin arziki na cikin mawuyacin hali kalubale mafi girma shine na rashin aikin yi.”




[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...