Gwamnatin Buhari ba ta ɗauki tsaro da muhimmanci ba—Bello Matawalle

Karamin ministan tsaro, Bello Matawalle, ya ce gwamnatin da ta gabata karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ba ta dauki batun rashin tsaro da muhimmanci ba.

Matawalle wanda ya gurfana gaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin tsaro tare da ministan tsaro, Abubakar Badaru, ya bayyana cewa ma’aikatar tsaro ta dauki sabbin jirage masu saukar ungulu don bunkasa yaki da rashin tsaro a kasar nan.

Hakan na zuwa ne kamar yadda Ministan Tsaro ya shaida wa kwamitin cewa akwai hadin kai a tsakanin Hafsoshin Tsaro na yanzu.

Mattawlle, yayin da yake magana a gaban kwamitin majalisar dattawa kan tsaro, ya ce batun rashin tsaro na bukatar kulawar hadin gwiwa daga jihohi, kananan hukumomi da na tarayya.

Ya ce, “A matsayina na tsohon Gwamnan Zamfara na san abin da na shiga a kan matsalar rashin tsaro, musamman ‘yan fashi da makami, wanda wani sabon salo ne a garemu a yankin Arewa maso Yamma.

“Batun Boko Haram ba sabon abu ba ne a yankin Arewa-maso-Gabas, amma saboda abin da ya faru a gwamnatin da ta shude, ba a magance matsalar da gaske ba.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...