Shugaba muhammadu Buhari ya bayana matukar kaduwarsa game da kisan da aka yi wa sojojin kasar a harin da mayakan Boko Haram suka kai wa kauyen Metele da ke jihar Borno.
Sai dai ya ce gwamnati ta dauki matakan gaggawa wajan ganin ba a sake maimaita kuskure irin wannan ba , da ya yi sanadin mutuwar sojojin.
A cikin sanarwar da ke dauke da sa hannun mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin manema labarai, Garba Shehu ,Shugaba Buhari ya ce gwamnatinsa za ta cigaba da ba batun tsaro fifiko domin tabbatar da tsaron lafiyar sojojin kasar da kuma na alummar kasa bakidaya.
‘Ba bu wani shugaban hafsan hafsoshi da zai zauna wuri daya, ba tare da daukar mataki ba yayin da ‘yan ta’ada ke jefa rayuwar sojoji da kuma alumma cikin hadari. Dakarunmu sun nuna karfinsu a kan ‘yan ta’adda kuma a shirye mu ke mu basu duk wani goyon baya da suke bukata wajan samar masu da makamai da karin sojoji domin su yi nasara wajan kawo karshen sabuwar barazanar da ake fuskanta daga Boko Haram.” in ji shi.
Ya kuma kara da cewa a kwanakin da ke tafe zai tattauna da shugabannin sojoji da kuma na leken asiri a kan matakan da zasu dauka
Sai dai shugaba Buharin ya yi la’akari da cewa yakin da ake yi da yan ta’ada ya shafi kasashen duniya shi yasa ake bukatar hadin kai tsakanin kasashe da ke fuskantar kalubalen tsaron irin wannan.
Ya kuma ba ‘yan Najeriya tabbaccin cewa gwamnatinsa ta dukufa wajan tabbatar da tsaronsu.
Sai dai ya yi kira ga ‘yan Najeriya a kan kada su saka siyasa a cikin abin takaicin da ya shafi kasa bakidaya, yana mai cewa mambobin rundunar sojin kasar tsintsiya madaurinki daya ce kuma manufarsu ita ce ce tabbatar da tsaron lafiyar yan kasa baki daya.