Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma’aikatan jihar.

Sanwo-Olu ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake halartar shirin Politics Today, wani shiri na tattaunawa a tashar Channels TV.

“Ina farin cikin sanar da ku cewa mafi karancin albashi a Jihar Legas, wanda muka tattauna da kungiyarmu, yanzu ya zama N85,000,” in ji Sanwo-Olu, yayin da yake amsa tambayar da mai gabatar da shirin ya yi masa kan batun mafi karancin albashi.

Gwamnan ya bayyana cewa wannan adadin ba gasa ba ce da sauran jihohi, amma la’akari ne da ikon jihar wajen biyan albashin.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...