Gwamnan Kano ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar ya kuma sanar da sake naÉ—a, Muhammad Sanusi a matsayin Sarkin Kano.

Yusuf ya bayyana haka ne jim kaÉ—an bayan da ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautu ta jihar da majalisar dokokin jihar ta yiwa garambawul.

Gwamnan ya saka hannu ne akan dokar da misalin Æ™arfe biyar 05:10 a gidan gwamnatin jihar a yayin wani Æ™warya-Æ™waryan taro da ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da kuma shugaban majalisar dokokin jihar.

A shekarar 2020 tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya sauke Sanusi daga Sarkin Kano kana ya ƙirƙiro ƙarin wasu masarautu guda biyar.

Har ila yau gwamnan ya bawa sarakunan sauran masarautu huÉ—u da sabuwa dokar ta soke da su sauka daga muÆ™aminsu cikin sa’o’i 48.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...