Gwamnan Kaduna ya rage kudin karatun manyan makarantun jihar

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Uba Sani, ya sanar da rage kudin makaranta na dukkanin manyan makarantun jihar.

Gwamnan ya sanar da haka a lokacin wani taro da yan jarida a gidan gwamnatin jihar dake Kaduna.

A cewar, Muhammad Lawal Shehu mai magana da yawun gwamnan ya rage kudin makarantar ne domin cika alkawarin yakin neman zabe da gwamna Uba Sani ya yi wa al’ummar jihar Kaduna.

Ya ce an dauki matakin ne biyo bayan korafe-korafen jama’a kan tsadar kudin makarantar da yadda yake shafar yawan daliban dake shiga makarantun da kuma wadanda suke dorewa da karatun bayan sun shiga ciki.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...