Haka zalika a jiya litinin dan majalisar wakilai dake wakiltar karamar hukumar Igabi inda lamarin ya auku, Zayyad Ibrahim ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ya zuwa yanzu dai ba’a tabbatar da hakikanin wadanda suka mutu ba, ya kuma ce ba mamaki adadin ya karu domin masu kai agaji na kan gudanar da aikinsu.
‘Zayyad ya kuma ce ‘yan bindigar sun fara da harbe-harbe ne akan jama’a bayan fitowar su daga masallaci, ya kuma kara da cewar wadanda suka raunata an kaisu wasu asibitocin dake yankin.
Shi kuwa Kansila Dayyabu Kerawa, ya ce wannan harin na mai da martini ne akan wani hari da sojojin Najeriya suka kai kan ‘yan bindiga a yankin.