
Gwamnan jihar Filato,Caleb Mutfwang ya karbi katin shiga jam’iyar APC bayan da ya fice daga jam’iyarsa ta PDP.
Mutfwang ya karbi katinsa na jam’iyar APC a ranarĀ Juma’a a wurin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar da aka yi a Jos babban birnin jihar.
Gwaman ya ce bukatar samar da ingantaccen shugabanci,alkiblar da ta dace da kuma saita jihar Filato ta yi dai-dai da shirye-shirye da tsare-tsaren gwamnatin tarayya ne ya saka shi daukar matakin sauya shekar zuwa jam’iyar APC.
Mutfwang ya godewa jam’iyar PDP kan damar da ta bashi har ya lashe zaben gwamnan jihar a shekarar 2023 da kuma goyon bayan da yan jam’iyar suka ba shi har ya zuwa wannan lokacin.

