Yayin da ake ci gaba da jin labarin sauya sheƙar wasu gwamnonin jihohi zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya bayyana cewa yana nan daram a jam’iyyarsa ta PDP.
Gwamnan ya yi wannan bayani ne bayan jita-jitar da ake yaɗawa cewa yana shirin komawa jam’iyyar APC.
Ya musanta rahotannin ne ta bakin shugaban jam’iyyar PDP a jihar Bauchi, Pharmacist Sama’ila Adamu Burga, a wata hira da BBC ta yi da shi.
Burga ya ce batun sauya sheƙar gwamnan ba gaskiya ba ne, yana mai jaddada cewa jita-jita ce kawai da ba ta da tushe.
Gwamnan Bauchi Ya Musanta Rade-raɗin Sauya Sheka Zuwa APC

