Gwamna Ya Maniyata Aikin Hajji Daga Bauchi Sun Samu Tallafin Dubu 900,000

Gwamnan jihar Bauchi,Bala Muhammad ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar ragin ₦900,000 kan kuɗi aikin da za su biya.

Muhammad ya sanar da haka ne cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Sanarwa ta ce an É—auki matakin ne la’akari da kuncin rayuwa da kuma matsi da ake fama da shi.

Kuɗin da gwamnan ya bawa maniyatan na nufin kaso 50 cikin 100 na ƙarin da Hukumar Aikin Hajji Ta Ƙasa NAHCON ta yi kan kuɗin kowace kujera.

“La’akari da halin kunci da tsadar rayuwa da muka tsinci kan mu a ciki, na sanar da biyan rabin karin kudin da hukumar kula da jin dadin alhazai ta kasa wato NAHCON ta bukaci kowane maniyyaci ya biya.”a cewar sanarwar

“Na biya wa kowane maniyyacin jihar Bauchi tallafın naira dubu dari tara da hamsin, wato kaso 50% na karin kudin, sannan na umurci hukumar a matakin jiha da ta mayar wa kowane maniyyaci kwatan-kwacin tallafın da muka biya, wadanda ba su biya karin ba kuma su cire kafın cikar wa’adin da aka diba.”

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...