Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres, ya yi Allah wadai da abin da ya bayyana a matsayin nuna wariya ga Musulmi a sassa daban-daban na duniya.
A cikin saƙon da ya fitar domin bikin Ranar Yaƙi da Ƙyamar Musulunci ta Duniya da ake gudanarwa a ranar 15 ga Maris, Guterres ya ce Musulmai na fuskantar matsaloli iri-iri a rayuwarsu ta yau da kullum.
“Musulmai a sassan duniya sau da yawa suna fuskantar nuna wariya daga hukumomi, da cire su daga harkokin tattalin arziki da zamantakewa, da tsauraran manufofin shige da fice, da kuma sanya musu idanu da bincike ba tare da wani dalili mai ƙarfi ba,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga al’ummar duniya da su haɗa kai domin kare haƙƙin ɗan Adam da mutuncin kowa da kowa, ba tare da la’akari da addini ba.
Guterres ya yi gargadin cewa irin waɗannan halaye na nuna ƙiyayya na ƙara yawaita ne sakamakon kalaman da ke haifar da ƙin juna, wanda zai iya haddasa cin zarafi da tashin hankali a cikin al’umma.
“Sake jaddada aniyyar tabbatar da daidaito, haƙƙoƙin dan’adam, da martabar kowane mutum, ba tare da la’akari da addininsa ba,” ya ƙara da cewa.
Guterres Ya Yi Allah Wadai Da Nuna Wariya Ga Musulmi A Duniya

