Gobara ta yi ƙurmus da sansanin yan gudun hijira a Borno

Rahotannin da suke fitowa daga jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya na nuna cewa gobara tlalata dukiyoyi da wasu kayayyaki masu daraja a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke Muna a karamar hukumar Jere a jihar.

An ce gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Laraba.

Wajen da gobarar ta yi ɓarna ke nan

Jami’an Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), sun kai ziyarar tantance wuraren da lamarin ya faru.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tantance musabbabin tashin gobarar ba.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan wata gobara ta ƙone shaguna da dukiyoyi na miliyoyin naira a babbar kasuwar Gamboru da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...