Gobara ta lalata shaguna 150 a kasuwar Zaria

Rahotannin da muke samu na nuna cewa gobara ta lalata shaguna sama da 150 a kasuwar ‘Yan Katako da ke Sabon Gari, Zariya a Jihar Kaduna.

Gobarar ta tashi ne a ranar Laraba da misalin karfe 1 na dare kuma ta ci gaba da ci har zuwa wayewar garin.

Babban jami’in tsaro na kasuwar Hamisu Buhari ya bayyana cewa gobarar ta fara ne a lokacin da Kamfanin Wutar Lantarki na KEDCO na Kaduna ya maido da wutan lantarki, inda wata igiyar wutar lantarki ta fado a rufin daya daga cikin shagunan.

An ruwaito yana cewa, “A karshe na tuntubi hukumar kashe gobara a babbar kasuwar Sabon Gari. Sun ce in kawo musu mai. Sai da na kawo musu kafin suka zo wurin.”

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...