Gobara biyu da suka tashi a ƙananan hukumomin Bade da Karasuwa a jihar Yobe sun lalata dukiya ta miliyoyin naira.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) ta bayyana hakan a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Facebook.
A cewar hukumar, gobarar farko ta tashi ne da misalin ƙarfe 9:20 na dare ranar 4 ga Maris, 2026 a kasuwar Kara da ke gaban Jami’ar Tarayya ta Gashua.
Hukumar ta ce gobarar ta cinye tarin abincin dabbobi da itacen wuta, lamarin da ya lalata hajojin ’yan kasuwa cikin ƙanƙanin lokaci.
Ta ƙara da cewa duk da cewa ba a samu asarar rai ba, amma mutane da dama sun shiga cikin matsananciyar matsala ta tattalin arziki saboda yawancin iyalai na dogaro da kasuwancin wajen samun abin rayuwa.
A wani lamari dabam kuma, SEMA ta ce gobara ta tashi a kasuwar zagaye ta Karasuwa Garun Guna tare da ƙauyen Mattafari da ke kusa da ita da misalin ƙarfe 3:00 na rana ranar 5 ga Maris.
Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta ƙone shaguna uku da rumfunan kasuwa guda 12, inda aƙalla mutane 61 suka rasa hanyar samun kuɗin shiga.
SEMA ta ce tuni tawagogin tantancewa suka isa wuraren da gobarar ta auku domin nazarin barnar tare da bayar da shawarwari kan matakan gaggawa da na dogon lokaci.
Gobara Ta Lalata Kasuwanni Biyu A Jihar Yobe

