Wata gobara da ta tashi da sassafe a kauyen Ado dake karamar hukumar Karu ta jihar Nasarawa ta kone wasu yara uku yayan mutum guda.
Wani kamfanin Dillancin Labaran Najeriya dake yankin ya rawaito cewa gobara da ta jefa mazauna yankin cikin jimami ta kuma kone gidan kurmus.
NAN, ya tattara cewa gobarar da ba a san musabbabinta ba ta kama ne da misalin karfe 6:30 na safiyar ranar Asabar.
Amma kuma wani da ya ganewa idonsa abin da ya faru, Mista Cambrit Ayet, wanda ya yi asarar kaya a gobarar ya ce: “matata ita ce ta fara fitowa taga baƙin hayaki na fitowa daga dakin makota inda ta fara ihun wuta-wuta.”
Mutumin ya ce yana jin muryar matarsa ya garzaya yana kiran neman taimako da kuma ceto abokanan da suke zaman haya tare wanda a rashin saninsa basa cikin gidan sai yayansu kawai waɗanda suke bacci a daki lokacin da wutar take ci.
Ya cigaba da cewa dai-dai lokacin da suke kokarin balle kofar dakin domin su duba ko daganan wutar ta tashi kawai sai suka hangi makociyar tasu ta tawo.
“Yayin da ta ga mutane da kuma abinda yake faruwa kawai sai ta fara ihu tana yayana, ƴaƴana ana muka gane cewa yaran suna ciki,” ya ce.