Gobara ta kashe wasu yara uku tare da kona wani gida a jihar Nasarawa

Wata gobara da ta tashi da sassafe a kauyen Ado dake karamar hukumar Karu ta jihar Nasarawa ta kone wasu yara uku yayan mutum guda.

Wani kamfanin Dillancin Labaran Najeriya dake yankin ya rawaito cewa gobara da ta jefa mazauna yankin cikin jimami ta kuma kone gidan kurmus.

NAN, ya tattara cewa gobarar da ba a san musabbabinta ba ta kama ne da misalin karfe 6:30 na safiyar ranar Asabar.

Amma kuma wani da ya ganewa idonsa abin da ya faru, Mista Cambrit Ayet, wanda ya yi asarar kaya a gobarar ya ce: “matata ita ce ta fara fitowa taga baƙin hayaki na fitowa daga dakin makota inda ta fara ihun wuta-wuta.”

Mutumin ya ce yana jin muryar matarsa ya garzaya yana kiran neman taimako da kuma ceto abokanan da suke zaman haya tare wanda a rashin saninsa basa cikin gidan sai yayansu kawai waɗanda suke bacci a daki lokacin da wutar take ci.

Ya cigaba da cewa dai-dai lokacin da suke kokarin balle kofar dakin domin su duba ko daganan wutar ta tashi kawai sai suka hangi makociyar tasu ta tawo.

“Yayin da ta ga mutane da kuma abinda yake faruwa kawai sai ta fara ihu tana yayana, ƴaƴana ana muka gane cewa yaran suna ciki,” ya ce.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...