
Wani ginin bene mai hawa uku dake kan layina Adeniyi a Lagos Island ya ruguzo.
Akalla mutane uku mazauna gidan aka samu damar cetowa aka kuma garzaya da su asibiti jim kadan bayan ruguzowar ginin a ranar Alhamis.
Gbenga Omotoso, kwamishinan yada labarai na jihar shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wani sako da ya wallafa a Facebook inda ya ce ba a tabbatar da musabbabin rushewar ginin ba.
“Ginin bene mai hawa uku ya ruguzo a Lagos Island, ” a cewar sakon da ya wallafa.
Ya kara da cewa jami’an aikin ceto na cigaba da bincike baraguzan ginin ko za su gano karin wasu mutanen da abun ya shafa.