Garkuwa da mutane: majalisar dattawa ta gayyaci babban sifetan ƴansanda

Majalisar dattawa ta gayyaci babban sifetan ƴansanda na kasa, Muhammad Adamu kan ayyukan masu garkuwa da mutane da kuma barayi masu ɗauke da makamai dake cigaba da cin karensu a sassa daban-daban na kasarnan.

Ana sa ran babban sifetan zai bayyana gaban majalisar a mako mai zuwa.

Majalisar ta tsayar da matakin gayyatar babban sifetan ne biyo bayan wani kudiri da sanata, Shehu Sani ya gabatar a zaman majalisar na ranar Alhamis.

Sani ya gabatar da kudirin ne biyo bayan kisan wata ma’aikaciyar agaji yar kasar Birtaniya, Faye Mooney da abokin aikinta, Matthew Oguche a wani gidan shakatawa dake Kajuru a jihar Kaduna.

Dukkansu sun mutu yayin musayar wuta tsakanin masu garkuwa da mutane da kuma yansandan kwantar da tarzoma dake gadin wajen.

More from this stream

Recomended