[ad_1]
Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya tallafawa matasa 15,400 a kokarin karfafa musu gwiwa na su rike kananan sana’o’insu.
Wadanda suka amfana da tallafin sun haɗa da maza 8,800 da kuma mata 6600 da ka zabo daga cikin ƙananan hukumomi 44 dake jihar.
Kowane namiji da ya amfana ya samu tallafin kudi ₦20,000 ya yin da ko wace mace za ta karbi ₦15,000.
Matasan da suka amfana da shirin sun haÉ—a da, wanzamai, mahauta,teloli, masu yin sabulu, masu tuyar kosai da kuma masu tallan abinci.
[ad_2]