Fiye Da Mutum 3,300 Sun Mutu A Yaƙin Iran


Hukumomin Iran sun bayyana cewa fiye da mutum 3,300 ne suka rasa rayukansu tun bayan ɓarkewar yaƙi tsakanin ƙasar da Amurka da kuma Isra’ila.

Alƙaluma daga sashen lafiya na ma’aikatar shari’ar ƙasar sun nuna cewa an riga an gano gawarwaki 3,375 zuwa yanzu.

Rahoton ya ce daga cikin waɗanda suka mutu, 2,875 maza ne, yayin da 496 mata ne.

Lardunan Tehran da Hormozgan da Isfahan ne suka fi fuskantar asarar rayuka a rikicin.

Haka kuma, rahoton ya nuna cewa ɗaruruwan yara na daga cikin waɗanda suka mutu. Ciki har da jarirai bakwai ‘yan ƙasa da shekara ɗaya, da yara 255 masu shekara ɗaya zuwa 12, da kuma 121 masu shekara 13 zuwa 18.

Bugu da ƙari, an ce wasu daga cikin waɗanda suka rasa rayukansu sun haɗa da ‘yan ƙasashen Afghanistan da Siriya da Turkiyya da Pakistan da China da Iraƙi da kuma Lebanon.

More from this stream

Recomended