
Fasinjoji da dama sun tsallake rijiya da baya dai-dai lokacin da babbar motar hayar da suke ciki ta kama da wuta a yankin Maryland na jihar Lagos.
Wani shedar gani da ido ya ce motar ta taso ne daga Ikorudu akan hanyarta ta zuwa yankin CMS na birnin lokacin da lamarin ya faru.
Diraben motar da kuma yaron motar sun yi gaggawar tserewa daga wurin.
Jami’an kai ɗaukin gaggawa da suka haɗa da ƴan sanda na hukumar sufuri ta jihar Lagos LASTMA da na hukumar kashe gobara sun yi gaggawar isa wurin.
Wata fasinja dake cikin motar ta bayyana cewa gobarar ta fara ne da hayaƙi daga ɓangaren direban motar kuma da farko fasinjojin motar sun zata hayakin yana fitowa daga wata motar ta daban ne.
“Amma kuma hayakin dake fitowa kadan sai ya ta’azzara nan danan kuma ya jefa mu cikin rudani,” a cewarta.
“Muna ganin hayakin yana ƙara yawa sai muka gaggauta ficewa daga motar kafin wutar ta tashi.”
Ta kara da cewa wasu daga cikin fasinjojin sun samu raunuka a yayin da suke ƙoƙarin ficewa daga motar.