Jagoran ɗariƙar Katolika na duniya, Fafaroma Leo, ya sake kira ga shugaban Isra’ila Isaac Herzog da a buɗe ƙofa domin kawo ƙarshen yaƙin Iran.
Rahoton kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce Fafaroman ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawar waya da suka yi da juna.
A cewar fadar Vatican, Fafaroma Leo, wanda ya dade yana sukar rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya, ya buƙaci Mista Herzog da ya tabbatar da kariya ga fararen hula tare da mutunta dokokin ƙasa da ƙasa da kuma na jin ƙai.
Kiran na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar tashin hankali a yankin, wanda ya janyo damuwa daga kasashen duniya.
Fafaroma Leo Ya Bukaci Isra’ila Ta Taimaka Wajen Kawo Karshen Yakin Iran

