Facebook zai fara nuna La Liga kai-tsaye kyauta

[ad_1]

La liga

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Kamfanin Facebook ya sanar da matakin fara nuna wasannin gasar La Liga ta Spain kai-tsaye kuma kyauta a wasu kasashen kudancin Asiya.

Za a fara kallon wasannin na kwallon kafa kai-tsaye a kafar Facebook a kyauta bayan kamfanin na sada zumunta ya sanar da kulla yarjejeniya da hukumar gasar La Liga ta Spain.

Wata sanarwa da kumar La Liga ta fitar ta ce Facebook zai nuna dukkanin wasannin gasar 380 na kakar bana da za a soma a ranar Juma’a.

Masu amfani da Facebook da ke sha’awar kwallon kafa za su kalli wasannin a kasashen India da Afghanistan da Bangladesh da Nepal da Maldives da Sri Lanka da kuma Pakistan.

Facebook zai ci gaba da nuna wasannin kai-tsaye daga wannan kakar har zuwa kakar wasanni biyu masu zuwa, a karkashin yarjejeniyar.

Facebook ya ce zai fara nuna wasannin ne ba tare da saka wata talla ba.

Sai dai kuma gasar ta La liga da kuma kamfanin na facebook ba su bayyana kudin da suka amince ba na yarjejeniyar.

Ana ganin wannan babban mataki ne ga Facebook na nuna wasannin gasar kwallon kafa. Kuma duk da cewa kasashen yankin sun fi sha’war kwallon kuriket da kuma wasannin kwallon kafa na Firimiyar ingila amma kuma sha’war kwallon kafa na ci gaba da karuwa a yankin musamman a India.

Ana dai ganin nuna wasannin kyauta da Facebook zai yi zai kashe wa wasu kafofin da ke nuna wasanni, musamman kamfanin Sony da aka ruwaito ya biya dala militan 32 don ‘yancin nuna wasannin gasar La Ligar Spaniya a yankin tsakanin shekarar 2014 zuwa 2018.

Facebook na da mabiya mliyan 348 a India da kudancin Asiya.

Kuma fara nuna wasannin kwallon kafa a shafukan sada zmunta na intanet kai tsaye kuma kyauta, wasu na ganin babbar barazana ce ga masu ‘yancin nuna wasannin kwallon kafa a kafofin talabijin.

[ad_2]

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...