
Gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i ya baiwa daukacin mayan jami’an gwamnatinsa umarnin sadaukar da kashi 50 na albashinsu domin tallafawa marasa karfi a jihar.
Gwamnan ya bayyana haka ne ta hannun Kakakinsa Muyiwa Adekeye, wadanda umarnin ya shafa, sun hada da kwamishinoni, sakatarorin din-din-din, masu bada shawara na musamman, da kuma shugabannin hukumomi a jihar.
Sanawar ta kuma yi karin bayanin cewar, gwamna El-Rufa’i ya baiwa daukacin mukarraban nasa umarnin bada tallafin naira dubu 500 kowannensu cikin wannan wata na Afrilu, domin tallafawa marasa karfi.
Kazalika manyan jami’an gwamnatin za su rika sadaukar da rabin albashinsu a kowane wata har sai an janye dokar hana jama’a fita.
El-Rufa’i ya bada umarnin ne kwana guda bayan kara wa’adin dokar hana fita da kuma zirga-zirga zuwa ciki da wajen jihar Kaduna da tsawon kwanaki 30.