EL-Rufai ya rattaba hannu kan dokar yi wa masu fyade dandaƙa

Nasiru El-Rufai

Bayanan hoto,
Gwamnan Jihar Kaduna Nasiru El-Rufai

Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya rattaba hannu kan dokar hukunci mai tsanani a kan duk wanda a ka kama da laifin fyade.

Dokar ta ba da damar kisa ko yin dandaka ga duk wanda a ka kama ya yi wa kananan yara ‘yan kasa da shekaru sha hudu fyade.

Hakama karkashin dokar za a iya yanke musu hukuncin daurin rai-da-rai.

Idan a ka kama mace kuwa dokar ta ce za a cire mata wani sashe na al’aura da ake kira Fallopian tube ko kuma a kashe ta.

Nasir el-Rufai ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa tabbas ya rattaba wa dokar hannu.

A makon da ya gabata ne majalisar jihar Kaduna ta amince da kudurin dokar.

Bugu da kari duk baligin da a ka kama da laifin yiwa ‘yan kasa da shekara 14 fyade, za a saka sunan shi kundin rajistar wadanda suka aikata fyade tare da wallafa su a kafafen yada labarai.

Kawo yanzu jihar Kaduna ce kawai a Najeriya da ta tanadi hukunci mai tsanani kan masu aikata fyade a Najeriya.

A na samun koke sosai kan fyade a watannin nan a Najeriya a yan watannin nan.

Kuma duk da hukumomi na samun nasarar kama masu aikata fyaden, ba kasafai a ke yanke musu hukunci ba.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...