![](http://arewa.ng/wp-content/uploads/image_editor_output_image-2083475639-16590415724947120523025012520116.jpg)
Hukumar EFCC dake yaki da masu yi wa tattalina arzikin kasa ta’annati ta samu nasara kama wasu mazabanta ta hanyar Intanet wadanda aka fi sani da yan Yahoo-Yahoo.
Jam’ian hukumar na shiyar Abuja su ne suka samu nasarar kama mutanen a yankin FO1 dake Kubwa a Abuja biyo bayan bayanan sirri da suka samu kan ayyukansu.
Mutanen da aka kama su 9 sun hada da kalu Kennedy Ndukwe, Onyenso Emmanuel, Richard Yakubu, Haruna Abubakar, Peter Ukabam, Godwin Peters, Usuman Garba Haruna, Nwani Chukwuma da kuma Kabiru Shehu.
Kayayyaki daban-daban aka samu a hannun mutane da suka hada da laptop da wayoyin hannu.