EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo bisa laifukan da suka shafi tattalin arziki da kuma kudi.

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook ranar Alhamis.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ana sanar da jama’a cewa Yahaya Adoza Bello (tsohon gwamnan jihar Kogi), wanda hotonsa ya bayyana a sama hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa na nemamsa ruwa a jallo bisa zargin karkatar da kudade har N80,246,470,089.88.

“Bello, dan shekara 48, ɗan kabilar Ebira ne kuma dan asalin karamar hukumar Okenne ne ta jihar Kogi.”

More from this stream

Recomended