DSS Ta Kama El-Rufai Jim Kaɗan Bayan EFCC Ta Ba Shi Beli

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (SSS) ta kama tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a daren Laraba jim kaɗan bayan da Hukumar EFCC ta sake shi kan beli.

Tun ranar Litinin EFCC ke tsare da shi bisa zargin cin hanci da rashawa. An ba shi beli da misalin ƙarfe 8 na dare.

Shaidu sun ce jami’an SSS masu ɗauke da makamai sun yi masa kwanton bauna a harabar hedikwatar EFCC, inda suka kama shi nan take bayan fitowarsa.

Daga nan ne aka tafi da shi zuwa hedikwatar SSS da ke yankin Asokoro a Abuja. Har yanzu babu tabbacin lokacin da za a sake shi.

Kamen nasa na da alaƙa da zargin da ake masa na saurarar wayar Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, ba bisa ƙa’ida ba.

A ranar Litinin ne SSS ta shigar da ƙarar laifukan yanar gizo a Kotun Tarayya da ke Abuja. Lamarin ya biyo bayan kalaman da El-Rufai ya yi a wata hira kai tsaye da gidan talabijin na Arise TV ranar Juma’a.

More from this stream

Recomended