Dr Ahmad Gumi Ya Yi Alhinin Rasuwar Ali Khamenei

Fitaccen malamin addinin Musulunci a Najeriya, Ahmad Mahmud Gumi, ya bayyana alhininsa kan mutuwar jagoran addinin Iran, Ali Khamenei.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Dr Gumi ya ce jagoran addinin ya yi sa’a ya rasu a matsayin shahidi.

“Ya mutu sakamakon harin waɗanda suka kashe ƙananan yara da matan da ba su ji ba su gani ba a Gaza da sauran wurare”, kamar yadda ya wallafa.

Malamin ya kuma bayyana Khamenei a matsayin jarumi, yana mai cewa jininsa zai haifar da sauyi ga al’umma.

“A tsaye yake don tabbatar da adalci, kuma ba ya ɓuya a ƙarƙashin ƙasa ba”, in ji shi.

Dr Gumi ya ƙara da cewa ga waɗanda suka kashe shi, “ga duniyar nan ya bar musu, sai su zuba ruwa a ƙasa su sha”.

More from this stream

Recomended