Dole Bukola Saraki ya bar majalisa —Akpabio

[ad_1]

Godswill Akpabio

Hakkin mallakar hoto
Facebook/ Godswill Akpabio

Tsohon gwamnan jihar Akwa-Ibom, Sanata Godswill Akpabio, ya ce dole shugaban majalisar dattawan Najeriya, Bukola Saraki ya bar majalisar idan ana son a kore shi daga majalisar.

Sanata Akpabio, wanda ya bar mukaminsa na shugaban marasa rinjaye a majalisar a lokacin da ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, ya fadi wannan maganar ce a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Abuja.

Saraki ya bi sawun wasu sanatoci da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP mara rinjaye lamarin da ya sa jam’iyyar APC mai rinjaye ke cewa ya kamata ya sauka daga shugabancin majalisar.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya ambato Akpabio yana cewar idan wasu suna neman a ayyana cewar babu kowa kujerar mazabarsa a majalisar saboda ya koma APC, dole Saraki da wadanda suka bar APC su ma su bar kujerunsu a majalisar.

Akpabio ya ce “duk wanda ya bar APC zuwa PDP, za mu ayyana kujerarsa a matsayin kujerar da babu kowa.”

Cikin ‘yan kwanakin nan dai an yi guguwar sauya sheka a siyasar Najeriya kamar yadda a aka yi gabannin zabukan 2015.

Hakkin mallakar hoto
Facebook/Bukola Saraki

Yayin da wasu ke ganin guguwar sauya shekar za ta iya tasiri kan yunkurin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na sake komawa kan karagar mulki a shekarar 2019, wasu gani suke sauye-sauyen shekar ba za ta hana Buhari komawa wa’adi na biyu ba.

[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...