Dokokin Haramta Luwadi: Sultan Na Brunei Ya Mayar Wa Jam’iar Oxford Digirin Karramawa Da Ta Ba Shi

Hassanal Bolkiah, Sultan na kasar Brunei, ya mayar wa Jami’ar Oxford digirin karramawa da ta ba shi saboda sukar da ya sha bayan ya kaddamar da hukuncin kisa kan ‘yan luwadi da ma’aurata mazinata a fadin Brunei.

Kusan mutum 120,000 ne suka rattaba hannu kan wani korafi na neman jami’ar da ta soke digirin da ta karrama shi da ita a shekarar 1993.

Jami’ar ta Oxford ta tabbatar da cewa dai Sultan din shi da kansa ya yi niyyar dawo masu da digirin.

A kwanakin baya ne dai Hassanal Bolkiah ya kaddamar da dokokin kisa kan duk wanda aka kama da laifin luwadi ko mai aure da aka kama yana zina.

Sai dai bayan kaddamar da dokar, Sultan din ya sha suka daga Majalisar Dinkin Duniya da ma taurari, cikinsu har da George Clooney.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...