Dogara ya mikawa jam’iyar PDP fom dinsa na sake tsayawa takara

Shugaban majalisar wakilai ta tarayya, Yakubu Dogara ya ziyarci sakatariyar jam’iyar APC dake Abuja bisa rakiyar wasu manyan yan siyasar jihar Bauchi a yau ranar Alhamis.

Yakubu Dogara ya yi amfani da ziyarar wajen sanar da ficewarsa daga jam’iyar APC mai mulki.

“Na yanke shawarar na dawo,” Dogara ya fadawa dandazon jama’ar da suka taru wadanda suke cikin murna.

Haka kuma ya mikawa jam’iyar fom dinsa na tsayawa takara a karkashin jam’iyyar da mutanen mazabarsa suka saya masa.

Tun lokacin da shugaban majalisa dattawa Abubakar Bukola Saraki ya fice daga jam’iyar ta APC masu lura da al’amuran yau da kullum ke ganin lallai Dogara shima zai fice daga jam’iyar ka wai dai yana jiran lokacin ya yi.

Sauya shekar tasa baya rasa nasaba da takun sakar dake tsakaninsa da gwamnan jiharsa ta Bauchi, Muhammad Abdullahi Abubakar.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...