‘Dodo’ Pogba ya taimaki Man Utd doke Leicester 2 -1

[ad_1]

Paul Pogba

Hakkin mallakar hoto
EPA

Image caption

Paul Pogba ya zura kwallo a wasansa na baya-bayan nan a gasar Rasha 2018

Kocin Manchester United Jose Mourinho ya yaba ma “dodo” Paul Pogba bayan da dan wasan ya jagoranci kungiyarsa ga nasara akan Leicerster City a ranar farko ta gasar firimiyar Ingila na bana, inda ya jefa kwallon farko.

Dan wasan da a kwanan nan ake rade-radin zai koma Barcelona ya bayar da mamaki, kwanaki hudu bayan da ya soma atisaye tun daworsa daga gasar cin kofin duniya da kasarsa Faransa ta lashe.

Man Utd ta fara wasan da kafar dama a filinsu na OLd Trafford, inda suka sami bugun daga kai sai gola bayan da Daniel Amartey ha taba kwallon da Alexis Sanchez ya buga da hannunsa.

Nan take Pogba ya aika da ita cikin ragar Leicester bayan wani bugu da yayi mai ban sha’awa, kuma gola Kasper Scmeichel bai iya tare ta ba.

Daga baya dan wasan baya na United, Luke Shaw ya jefa tasa kwallon bayan da ya yi nasarar gyara kuros din da Juan Mata ya aika cikin gidan Leicester.

Amma Leicester ma ta zura kwallo daya ta hannun Jamie Vardy wanda aka saka daga baya.

Pogba ya buga wasa na tsawon minti 84 kafin Marouane Fellaini ya maye gurbinsa.

Mourinho ya ce bai yi tsammanin Pogba zai iya dadewa a wasansa na farko ba:

“Pogba dodo ne. Mun yi tsammanin ba zai iya wuce minti 60 ba, amma sai ga shi ya wuce minti 80 ma.”

“The decision belonged to Paul. I asked him and he made himself available and he was very good.”

Mourinho ya kara da cewa, “Zabin cigaba da buga wasan na Pogba ne. Na tambaye shi ko zai huta, amma sai ya ce gara ya cigaba da buga wasan”.

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...