[ad_1]
Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata David Mark ya shiga takarar shugaban kasa inda ya yi alkawarin gyara tattalin arzikin.
Da yake wa shugabannin jam’iyar PDP jawabi jim kadan bayan da sayi fom din takarar shugabancin kasar nan, ranar Talata a sakatariyar jam’iyar dake Abuja.Mark ya ce kwarewar da ya samau aikin soja za ta da kara masa damar da yake da ita.
Ya yi ritaya daga rundunar sojan Najeriya a matsayin Birgediya Janar.
Mark ya ce duba da mutanen da suka sayi fom din takarar shugaban kasa a jam’iyar,” cikin ruwan sanyi zaka iya cewa jam’iyar PDP ce zabin jama’a,a kasarnan.”
A ranar Litinin da ta gabata ne mai magana da yawun tsohon shugaban majalisar dattawan ya sheda wa jaridar The Cable cewa akwai yiyuwar maigidansa ya tsaya takarar shugaban kasa.
[ad_2]