Daraktan gidan tarihin Auschwitz ya buƙaci Buhari ya yafe wa yaron da ya zagi Allah a Kano

A team of Islamic Sharia enforcers called Hisbah is on patrol in the northern Nigerian city of Kano in an open pickup. File photo

Bayanan hoto,
Jami’an hukumar Hisbah a Kano

Daraktan kula da gidan tarihin Auschwitz, tsohon sansanin ƴan Nazi a Poland ya yi tayin zaman gidan yari na hukuncin ɗaurin shekara 10 da aka yanke wa wani yaro ɗan Najeriya mai shekara 13 da ya zagi Allah a Kano.

Dakta Piotr Cywinski, ya ce shi da wasu ƴan sa-kai 119 daga sassan duniya za su yi wa yaron zaman gidan yari na wata ɗaya ko wannensu.

A watan Agusta ne kotun shari’ar musulunci ta yanke wa yaron hukunci kan wasu kalamansa da ba su dace game da Allah yayin wata muhawara da abokinsa a jihar Kano

Lauyan yaron ya ɗaukaka ƙara, yana cewa hukuncin ya saɓa wa ƴancin yara da kuma kundin tsarin mulkin Najeriya. Ya shaida wa BBC cewa har yanzu ba a sa ranar sauraren ƙarar da ya ɗaukaka ba a kotun.

Jihar Kano na ɗaya daga cikin jihohi 12 a Najeriya da ke bin tsarin gwama shari’ar musulunci da dokokin ƙasa.

Asusun kula da yara ƙanana na Majalisar Ɗinkin Duniya Unicef, ya yi kira ga hukumomin Najeriya su gaggauta sake duba hukuncin.

Me daraktan gidan tarihin Auschwitz Memorial ya ce?

A cikin wasiƙar da ya aika wa Shugaba Buhari, Dakta Cywinski, ya rubuta cewa a shirye yake ya yi wa yaron zaman gidan yarin.

“Ba tare da la’akari da abin da ya faɗa ba, ba za a iya ɗaukar shi mai cikakken hankali ba, saboda shekarunsa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa idan har ba za a yafe wa yaron ba, shi da wasu ƴan sa-kai 119 za su yi masa zaman gidan yarin.

Ya kuma ce za su ɗauki nauyin karatun yaron.

Gidan tarihin na Auschwitz bai cika tsoma baki ba a irin wannan batu.

Zuwa yanzu gwamnatin Najeriya ba ta ce komi ba game da batun

Gidan tarihin na Auschwitz-Birkenau, tsohon sansaani ne na ƴan Nazi a Poland inda aka kashe mutum miliyan ɗaya da dubu ɗari ɗaya, kuma kusan mutum miliyan ɗaya da aka kashe Yahudawa ne.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...