Darajar kudin Turkiyya na kara faduwa

[ad_1]

Mista Erdogan

Image caption

Shugaba Erdogan ya shaidawa ‘yan kasar faduwar darajar Lira tamkar wani abu ne ya fada cikin kofin shayi, ba duka ba ne ya zube

Darajar kudin Turkiyya Lira na ci gaba da faduwa cikin sauri idan aka kwatanta da kudaden kasashen waje, duk da cewa ministan kudin kasar Berat Albayrak ya sanar da daukar matakan ceto tattalin arzikin Turkiyya da ke fuskantar barazana.

Shugaba Racep Tayyep Erdogan ya shaidawa dandazon magoya bayansa a birnin Trabzon cewa Amurka ce ta janyowa kasarsa halin da suke ciki yanzu.

Ya sanar da cewa za a mai dawa wadanda suke yakin kasuwanci da kasashen duniya ciki har da Turkiyya martanin cewa ba za’a dawwama a haka ba.

Mista Erdogan ya kara da cewa”Za mu warware ta hanyar sabbin abokan huldar kasuwanci, idan kun lura sun kara haraji kan Tama da Karafa, ba za mu karaya ba dan mu ma mambobin kungiyar kasuwanci ta duniya ne”.

A ranar asabar da ta gabata shugaba Erdogan ya yi kira ga ‘yan kasar musamman mata da suke ajiyar kadarar gwala-gwalai, da su dauko su dan sauyawa zuwa kudin Lira da zuba kudin a bankuna dan ceton tattalin arzikin kasarsu.

Masu aiko da rahotanni sun bayyana cewa tuni hannayen jarin wasu kamfanonin kasar suka fara fuskantar koma baya, ya yin da masu zuba jari kuma su ka dan janye saboda rashin sanin halin da kasar za ta iya fadawa a ciki.

Masana tattalin arziki sun ce idan aka kara daukar makwanni ba tare da Lira ta fara farfadowa ba, farashin kayan amfanin yau da kullum musamman na abinci za su kara tashi abin da hakan ke nufin ‘yan kasar za su dandana kudarsu.

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...