Dan wasan Super Eagles zai yi wa Sakkwatawa kyauta kan Pillars

Abdullahi Shehu yana fatan Sokoto United za ta yi nasara a kan Kano Pillars

Abdullahi Shehu yana fatan Sokoto United za ta yi nasara a kan Kano Pillars

Dan wasan bayan tawagar kwallon kafa ta Najeriya, Super Eagles, Shehu Abdullahi ya yi alkawarin bai wa kungiyar kwallon kafa ta Sokoto United kyautar kudi idan suka ci Kano Pillars.

A wani sakon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Abdullahi ya yi alkawarin bai wa kulob din na Sokoto naira 100,000 kan kowace kwallon da ya ci idan ya samu nasara a kan kungiyar Kano Pillars.

Sokoto United za ta kara da Kano Pillars a wani wasa na gasar Aieto Cup wadda ake ce wa gasar kalubale.

Dan wasan, wanda a yanzu haka yana taka leda a kungiyar Bursaspor ta Turkiyya, ya ce ya dauki wannan matakin ne domin nuna goyon bayansa ga tsohon kulob dinsa.

Duk da cewa Abdullahi ya taba buga wa Kano Pillars wasa, dan wasan ya ce ya yi sakon bidiyon ne ga hukumar gudanarwa da kuma ‘yan wasan kungiyar Sokoto United.

Ya ce “ga duk wani kwallon da kuka ci kano Pillars tare da nasara, zan ba ku naira 100,000.

“Idan kuka ci kwallo biyu za ku samu 200,000, idan kuka ci uku za ku samu 300,000. Idan za ku iya cin biyar zuwa goma, zan ba ku kudinsu.”

Daga nan sai ya yi wa Sokoto United din fatan alkhairi a wasan.

Dan wasan dai ya yi wasa a Sokoto United da Kano Pillars da Qasida FC na Kuwait kafin ya koma taka leda a Turai.

Sokoto United dai ta fitar da MFM, da ke buga gasar Firimiyar Najeriya, a gasar kafin wannan karawar da za ta yi da Kano Pillars.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...