Dalilin da yasa na gana da Obasanjo -Saraki

[ad_1]








Shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana dalilin da yasa ya kai wa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ziyara a gidansa dake Abeokuta a jihar Ogun.

Da yake magana da manema labarai bayan ganawar sirrin da suka yi, ya ce ya ziyarci, Obasanjo ne saboda bai samu damar halartar wurin bikin bude dakin karatu da aka yi mai suna Olusegun Obasanjo Presidential Library.

Ya ce: “kunsan cewa ban samu damar halartar wurin bikin bude dakin karatun ba shi yasa yanzu na yanke shawarar zuwa na gani da ido na a zahirin gaskiya wurin ya kayatar.Muna alfahari da abinda ya yi anan.”

Lokacin da yan jaridu suka tambaye shi kan rikicin dake faruwa a majalisa da kuma yaushe majalisar za ta sake zama Saraki ya yi shiru inda ya shige cikin motarsa da sauri.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...