[ad_1]
Shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana dalilin da yasa ya kai wa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ziyara a gidansa dake Abeokuta a jihar Ogun.
Da yake magana da manema labarai bayan ganawar sirrin da suka yi, ya ce ya ziyarci, Obasanjo ne saboda bai samu damar halartar wurin bikin bude dakin karatu da aka yi mai suna Olusegun Obasanjo Presidential Library.
Ya ce: “kunsan cewa ban samu damar halartar wurin bikin bude dakin karatun ba shi yasa yanzu na yanke shawarar zuwa na gani da ido na a zahirin gaskiya wurin ya kayatar.Muna alfahari da abinda ya yi anan.”
Lokacin da yan jaridu suka tambaye shi kan rikicin dake faruwa a majalisa da kuma yaushe majalisar za ta sake zama Saraki ya yi shiru inda ya shige cikin motarsa da sauri.
[ad_2]