Dakarun Operation Safe Haven sun lalata wasu maboya da ake zargin na ’yan ta’adda ne tare da kwato makamai yayin wani sintiri na farmaki a dajin Yankari da kewaye, a ƙaramar hukumar Alkaleri ta jihar Bauchi.
Wani masani kan yaki da ta’addanci a yankin Tafkin Chadi, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a shafinsa na X. Ya ce an gudanar da aikin ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar 20 ga Maris, ta hannun dakarun rundunar 33 Artillery Brigade, a wani ɓangare na ƙoƙarin ci gaba da kawar da miyagun laifuffuka a yankin.
Makama ya bayyana cewa dakarun sun yi bincike a cikin dajin, inda suka gano maboyar da wuraren taruwar da ake zargin ’yan ta’adda na amfani da su.
Ya ce, “During the operation, troops successfully destroyed the identified hideouts and neutralised the threat within the general area,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an samu nasarar kwato bindigogi biyu kirar dane gun yayin aikin.
A cewarsa, an gudanar da wannan aiki ne domin hana ’yan ta’adda samun damar gudanar da ayyukansu cikin sauƙi, tare da dawo da tsaro a yankunan daji na jihar.
Dakarun Sojoji Sun Lalata Maboyar ’Yan Ta’adda A Bauchi, Sun Kwato Makamai

