Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa ‘yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Wani jagoran al’umma daga yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya tabbatar da kamen ga manema labarai.

Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a ranar Laraba, misalin ƙarfe 4:44 na yamma a kasuwar ƙauyen SCC bayan samun bayanan sirri da sojojin suka yi.

Ya bayyana cewa sojojin da ke tsayawa a hanyar Bishini, bayan sun samu bayanan sirri, sun nufi kasuwar suka kama waɗanda ake zargin yayin da suke siyan kayan abinci da sauran abubuwa a kasuwa.

Ya ƙara da cewa sojojin sun dade suna zargin waɗanda ake zargin, amma sai a ranar Alhamis suka cafkesu a kasuwa suna siyan kayan da ake zargin za su kai wa ‘yan bindiga a maboyarsu.

More News

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta ɗauki hanyar warware rikicin jam’iyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin...

An gano gawar wani jami’in tsaro a ɗakinsa a Abuja

A gano gawar wani mataimakin Sifiritandan Ƴan sanda  Musa Yakubu dake aiki da ofishin ƴan sanda na Yaba a karamar hukumar Abaji dake birnin...