Dakarun Iran Sun Ce Sun Kai Hari Na 48 Kan Isra’ila

Rundunar dakarun juyin juya hali na Iran ta ce ta ƙaddamar da hari na 48 kan Isra’ila, kamar yadda kafofin yaɗa labarai na ƙasar suka ruwaito.

Kamfanin dillancin labarai na Jamhuriyar Musulunci ya bayyana cewa an kai sabon harin ne tare da haɗin gwiwar mayaƙan ƙungiyar Hezbollah da ke ƙasar Lebanon.

Rikicin tsakanin Iran da Isra’ila tare da Amurka a gefe guda ya ɓarke ne kusan mako biyu da suka gabata, bayan da Amurka da Isra’ila suka kai hare-hare kan Iran. Rahotanni sun ce hare-haren sun yi sanadin mutuwar wani babban jagoran addini a ƙasar.

A matsayin martani, Iran ta ci gaba da ƙaddamar da hare-hare kan Isra’ila da kuma wasu sansanonin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

More from this stream

Recomended