
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa NCDC ta ce mutane 31 ne suka mutu a cikin makonni biyar sanadiyar kamuwa da cutar zazzabin Lassa.
Hukumar ta bayyana haka a cikin rahoton ta da saba fitarwa kan halin da ake ciki game da cutar inda ta ce an samu rahoton zargin kamuwa da cutar har guda 754 amma kuma guda 165 ne aka tabbatar cutar ce.
Rahoton ya ce ma’aikatan lafiya 9 ne aka tabbatar sun kamu da cutar.
” A 2026 jumullar jihohi 9 ne aka samu mutum guda dai-dai da ya kamu da cutar a ƙananan hukumominsu 33,” a cewar rahoton.
Kaso 92 cikin 100 na waɗanda aka samu na dauke da cutar sun fito ne daga jihohi biyar da suka hada da Bauchi, Ondo, Taraba, Edo da kuma jihar Filato.
Rahoton ya kara da cewa mutane yan rukunin shekaru 21-30 su ne waɗanda suka fi kamuwa da cutar.

