Buhari zai samu kuri’a miliyan 2.5 a jihar Katsina – Masari

Gwamnan jihar Katsina,Aminu Bello Masari, ya ce shugaban kasa Muhammad Buhari zai sami akalla kuri’a miliyan 2.5 daga jihar a shekarar 2019.

Masari ya fadi haka bayan da ya gana da shugaban kasa Muhammad Buhari a fadar shugaban kasa dake Abuja a ranar Alhamis.

Buhari wanda ya fito daga jihar ya samu ƙuri’u 1,345,441 a zaben shekarar 2015, jihar tana da mutane miliyan 2,827,943 da suka yi rijistar zabe, a wancan lokacin.

Ya zuwa watan Agusta hukumar zabe ta kasa, INEC ta bayyana cewa karin mutane 329,257 sabbi da ta yiwa rijista.

Da yake magana da masu dauko rahoto daga fadar shugaban kasa, gwamnan na Katsina ya ce mutanen jihar a shirye suke su kara yawan ƙuri’un da suka bawa shugaban kasa a zaben shekarar 2019.

“Mutanen Katsina suna bayan shugaban kasa Muhammad Buhari ɗari bisa ɗari kuma za su cigaba da goya masa baya har bayan kammala zaben 2019,” ya ce.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...