[ad_1]
Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Sanata Chriss Ngige ya ce shugaban kasa, Muhammad Buhari ya fi kaso 80 na mutanen kasarnan koshin lafiya.
Ngige ya bayyana haka a matsayin martani kan damuwar da wasu suke nunawa akan shekarun shugaban kasar da kuma lafiyarsa dama yadda zai shafi gudanar da ayyukansa.
Da yake magana da yan jaridu a Awka babban birnin jihar Anambra, Ngige ya ce a matsayinsa na likita zai iya cika baki kan lafiyar jikin shugaban da kuma ta ƙwaƙwalwarsa.
Ministan ya kwatanta Najeriya da kasar Malaysia, ya ce lokacin da kasar dake yankin Asia ta shiga cikin rudanin siyasa dana tattalin arziki ta dogara kan Mahathir bin Mahmud domin ya jagorance ta
“Wannan mutumin (Buhari) ya na cikin koshin lafiya fiye da kaso 80 na yan Najeriya.”
“Ni likita ne, zan iya fada maka cewa lafiyayye ne fiye da mutanen da suke ganin batun lafiyarsa abun damuwa ne.”
[ad_2]