Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya ce duk da gazawar Buhari wajen magance wasu matsaloli zai ci zaɓen shugaban kasa a shekarar 2019.Da yake magana a cikin shirin Siyasa Ayau na gidan Talabijin na Channels, Sani ya ce shugaban kasar ya samu nasarori da za su saka yan Najeriya su zabe shi.”Ban taba nuna shakku cewa shugaban kasa Muhammad Buhari zai lashe zabe a shekarar 2019 saboda na yarda cewa akwai nasarori da dama da za a iya jingina su da jagorancinsa na tsawon shekaru 3 da rabi, “Sani ya ce.”Haka kuma zamu iya ganin wasu kalubale da kuma rashin nasara a yan wasu ɓangarori.amma na yarda wadanda suka zabe a shekarar 2015 har yanzu sun yarda kuma suna da kyakkyawan fata akansa a matsayin wanda zai kai su tudun mun tsira.”