Buhari ya gaza a wasu fannoni duk da haka za a sake zabensa a 2019- Shehu Sani

Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya ce duk da gazawar Buhari wajen magance wasu matsaloli zai ci zaɓen shugaban kasa a shekarar 2019.Da yake magana a cikin shirin Siyasa Ayau na gidan Talabijin na Channels, Sani ya ce shugaban kasar ya samu nasarori da za su saka yan Najeriya su zabe shi.”Ban taba nuna shakku cewa shugaban kasa Muhammad Buhari zai lashe zabe a shekarar 2019 saboda na yarda cewa akwai nasarori da dama da za a iya jingina su da jagorancinsa na tsawon shekaru 3 da rabi, “Sani ya ce.”Haka kuma zamu iya ganin wasu kalubale da kuma rashin nasara a yan wasu ɓangarori.amma na yarda wadanda suka zabe a shekarar 2015 har yanzu sun yarda kuma suna da kyakkyawan fata akansa a matsayin wanda zai kai su tudun mun tsira.”

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...