A ranar Juma’a shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince da murabus din da ministar kudin Najeriya, Kemi Adeosun ta yi.
Haka kuma shugaban kasar ya amince da karamar ministar kasafin kudi da tsare-tsare, Zainab Ahmad ta cigaba da kasancewa mai rikon mukamin ministar kudi.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da, Femi Adesina mai magana da yawun shugaban kasar ya fitar.
A cikin wasikarta ta barin aiki tsohuwar ministar ta godewa shugaban kasar kan damar da ya bata na yin aiki tare shi.
Ta ce ba dagangan ta yi takaradar NYSC ta bogi ba inda ta bayyana yadda ta samu takardar.